DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An shiga rudani a kotun da’ar ma’aikata ta Nijeriya kan rikicin shugabanci

-

Tambarin Kotun da’ar ma’aikata 

Har yanzu tsugune ba ta kare ba a kotun da’ar ma’aikata ta Nijeriya CCT yayin da ake takun-saka tsakanin shugabanta, Danladi Umar da sabon shugaban da aka nada, Mainasara Kogo, waɗanda ko wannensu ke ayyana kan sa a matsayin shugaba. 

Binciken da jaridar Dailytrust ta yi ya nuna cewa mutanen biyu ko wanne ya je ya tattaunawa da ma’aikatan kotun ba tare da wani kwakkwaran umarni kan wane ne shugaba ba. 

A ranar 13 ga watan Yuli ne shugaba Bola Tinubu ya nada Kogo a matsayin sabon shugaban kotun ta CCT, kazalika a wannan rana ce ya bayyana Omolola Oloworaran a matsayin Darakta Janar na Hukumar Fansho ta Kasa wato PENCOM. 

Su dai ma’aikatan sun koka kan yadda ake tafiyar da aikin kotun tun bayan da aka fara cece-ku-ce kan batun tsige Danladi Umar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara