DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon kwamishinan Ganduje ya soki gwamnatin Abba bisa zargin sayar da filin makarantar

-

Tsohon kwamishinan ilimi na a zamanin Ganduje, Muhammad Sanusi Sa’id Kiru, ya soki matakin gwamnatin Abba Kabir Yusuf na mayar da Makarantar Sakandare ta ‘Yan Mata GGSS Maikwatashi zuwa Kaura Goje, yana mai cewa an yi hakan ne cikin son rai.

A wata wasika da ya rubuta wa Gwamnan, tsohon kwamishinan ya bayyana cewa, duk da yana goyon bayan kudirin gwamnatin na inganta harkar ilimi, yadda aka gudanar da wannan aiki ya nuna rashin kwarewa da kuma rashin tsari daga masu ruwa da tsaki.

Google search engine

Ya ce rusa tsohuwar makarantar kafin a kammala sabuwar ya haifar da matsaloli ga dalibai da malamai da mazauna yankin.

Kiru ya kuma soki abin da ya kira da sayar da filin makarantar Maikwatashi a kan Naira miliyan 100 kowace gona, yana mai cewa wannan mataki ba daidai ba ne kuma ya saba da walwalar al’umma.

A cewarsa, filin ya kamata a mayar da shi wajen gudanar da ayyukan al’umma kamar filin motsa jiki, dakin taro ko cibiyar koyar da sana’o’i.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaban Amurka Donald Trumph ya haramtawa Farfesa Wole Soyinka zuwa kasar

Gwamnatin Amurka karkashin jagorancin shugaba Donald Trump ta soke takardar izinin shiga ƙasar ga Farfesa Wole Soyinka, sanannen marubuci a duniya. Farfesa Soyinka ya bayyana hakan...

Hukumar agajin gaggawa NEMA ta karɓi ƴan Nijeriya 153 da suka makale a Chadi

Hukumar ba da agajin gaggawa ta Nijeriya NEMA, ta bayyana cewa ta karɓi ’yan Nijeriya 153 da suka dawo daga ƙasar Chadi, ƙarƙashin shirin Ƙungiyar...

Mafi Shahara