Jam’iyyar PDP ta ce za ta daukaka kara kan hukuncin kotun tarayya da ta dakatar da gudanar da babban taronta da aka shirya yi a Ibadan, jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba.
A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar a ranar Juma’a, PDP ta bayyana hukuncin a matsayin kutse ga tsarin dimokuradiyya, tana mai jan hankalin mambobinta da su ci gaba da shirin taron ba tare da rudani ba.
Jam’iyyar ta ce ta umarci lauyoyinta su daukaka kara nan take, tare da jaddada cewa hukuncin bai hana ta ci-gaba da shirye-shiryen gudanar da taron da zai zabi sabbin shugabannin jam’iyyar ba, domin ci-gaba da kare dimokuradiyya a Nijeriya.
