Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAmurka ta mayar wa China da martani kan gargadin harin soja a...

Amurka ta mayar wa China da martani kan gargadin harin soja a Nijeriya

Wani ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya caccaki China saboda gargadin da ta yi wa Washington kan yiwuwar harin soja a Nijeriya bisa zargin kisan Kiristoci, yana mai cewa Beijing ba za ta tsoma baki a siyasar Amurka ba.

Moore ya goyi bayan shugaba Donald Trump, yana mai cewa Amurka na da nauyin kare Kiristoci masu fuskantar zalunci, kuma ya zargi China da rashin gaskiya kan batun ‘yancin dan Adam, yana cewa ba za a karɓi nasiha daga “gwamnatin kama-karya” ba.

China ta gargadi Amurka da ta daina tsoma baki a harkokin tsaron Nijeriya, inda ta bayyana goyon bayanta ga gwamnatin Nijeriya.

Sai dai gwamnatin kasar China, ta gargaɗi Trump da ya mutunta ikon da ‘yancin Nijeriya, tare da kauce wa duk wani yunkurin tura sojojin Amurka zuwa ƙasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata