DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ci-gaban tattalin arzikin Nijeriya bai kawo saukin rayuwa ga ‘yan kasar ba – Sanusi Lamido Sanusi

-

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya gargadi cewa ci-gaban tattalin arzikin Nijeriya ba ya fassaruwa zuwa ingantacciyar rayuwa ga ’yan ƙasar.

Sanusi ya bayyana hakan ne a wani taron kasa da kasa na Afirka kan kudin Musulunci da aka gudanar a Legas, inda ya ce ƙididdigar ci-gaban tattalin arziki da hauhawar farashi ba su nuna ainihin halin da talakawa ke ciki ba.

Google search engine

A cewarsa, duk da cewa GDP na ƙaruwa, idan ya takaita ne ga wasu kawai, yawancin jama’a za su ci gaba da fama da talauci.

Sanusi ya shawarci cibiyoyin kuɗin Musulunci da su mai da hankali wajen tallafawa kananan ’yan kasuwa, manoma da ma’aikata a yankunan karkara, yana mai cewa hakan ne kaɗai zai tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An fitar da jihohi 4 a Gasar Kokawar Nijar ta 2025

Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda...

Ya kamata a canza salon yadda ake yakar ‘yan bindiga a Nijeriya

Daga: Farfesa Usman Yusuf Litinin : 22 Disamba 2025 Ban taɓa gudu ko ja da baya ba ko nuna wata fargaba wajen bayyana matsayina a kan yaƙin...

Mafi Shahara