DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar alhazan Nijeriya ta kammala duba gidajen saukar alhazai a Madina don aikin hajjin 2026

-

Hukumar alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta bayyana cewa ta kammala duba wuraren saukar alhazai da masu samar da abinci a birnin Madina a cikin shirin farkon da take yi na gudanar da aikin hajji na shekarar 2026.

Wannan bayani na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban hukumar ta fuskar yada labarai, Ahmad Muazu, ya fitar a ranar Juma’a.

Google search engine

A cewar Muazu, kwamitin ya duba sama da otal 20 da wuraren dafa abinci guda bakwai a yankin markaziyya, inda suka tabbatar da bin ƙa’idojin tsaro, tsafta da sharuddan hukumar.

Hukumar ta NAHCON ta bayyana cewa za ta cigaba da tabbatar da cewa dukkan alhazai daga Nijeriya suna samun ingantaccen ayukka da ya dace da kuɗin da aka biya, tare da ƙarfafa tsare-tsaren da ke tabbatar da gaskiya da inganci wajen hidimomin aikin Hajji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Manyan Arewa za su tattauna yadda za a shawo kan matsalar tsaro a yankin

An shirya gudanar da babban taron tsaro a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, a ranar Litinin, 10 ga Nuwamba, 2025, domin tattauna hanyoyin magance...

Gwamnan Neja ya sallami shugaban hukumar SUBEB daga aiki

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya kori shugaban hukumar ilimin firamare ta Jiha (SUBEB), Muhammad Baba Ibrahim, tare da dukkan mambobin dindindin na hukumar. Sanarwar...

Mafi Shahara