Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Tinubu ta kaddamar da shirin ba da bashi ga ma'aikatan manyan...

Gwamnatin Tinubu ta kaddamar da shirin ba da bashi ga ma’aikatan manyan makarantu kasar

Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da ba da bashin Naira miliyan 10 ba tare da ruwa ba a karkashin shirin tallafa ma ma’aikatan manyan makarantu (TISSF), domin karfafa guiwa da inganta walwalar ma’aikatan manyan makarantu a fadin kasar.

Ministan Ilimi na Nijeriya, Tunji Alausa, ya bayyana haka a bikin kaddamar da shirin a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Akure (FUTA), inda ya ce wannan mataki wani muhimmin bangare ne na ajandar Renewed Hope ta shugaban Nijeriya Bola Tinubu, wacce ta mayar da hankali kan ci-gaban ilimi da habaka jarin jama’a.

Shirin yana bai wa ma’aikata damar samun bashin har zuwa Naira miliyan 10 ba tare da ruwa ba, don tallafawa bukatu irin su gina gida, kula da lafiya, sufuri da kananan sana’o’i.

Fiye da ma’aikata 9,000 daga manyan makarantu 219 na jihohi da na tarayya sun riga sun karɓi wasiƙar amincewa, inda fiye da mutum 400 suka samu kudinsu.

Alausa ya yi kira ga wadanda suka ci gajiyar shirin da su biya cikin lokaci domin tsarin ya cigaba da taimakawa wasu, yayin da gwamnati ta tabbatar da cewa gaskiya, bin doka da kulawa a kowane lokaci za su kasance ginshikan nasarar shirin nan gaba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata