Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnatin Nijeriya za ta cigaba da taimaka ma ‘yan gudun hijira da...

Gwamnatin Nijeriya za ta cigaba da taimaka ma ‘yan gudun hijira da masu karamin karfi – Ministan jin kai

Ministan jin kai da rage talauci Bernard Doro, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya da ke cikin mawuyacin hali cewa gwamnati tana da cikakken kudiri na taimaka musu da kuma tabbatar da tsaron rayukansu.

Yayin da yake zantawa da manema labarai a Jos a ranar Litinin, Doro ya ce manufar ma’aikatarsa ita ce tabbatar da cikar buri ga talakawa, masu gudun hijira, da sauran marasa galihu.

A cewarsa, ma’aikatar za ta inganta tsarin tallafi, fadada damar samun shirye-shiryen rage talauci, tare da tabbatar da cewa taimakon jin kai yana isa ga wadanda suka fi bukata.

Ministan ya kara da cewa gwamnati za ta aiwatar da ayyukan jin kai ba a matsayin taimako ba, sai a matsayin hakkin da gwamnati ke da shi ga ‘yan Nijeriya, domin tabbatar da abinci, ilimi, da mafaka ga marasa karfi.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata