Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaKotu ta sake bayar da umarnin dakatar da babban taron jam'iyyar PDP...

Kotu ta sake bayar da umarnin dakatar da babban taron jam’iyyar PDP na kasa

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sake hana jam’iyyar PDP gudanar da taron gangamin ta na kasa da aka shirya yi a Ibadan, Jihar Oyo, daga ranar 15 zuwa 16 ga watan Nuwamba.

Kotun ta kuma hana hukumar zabe ta Nijeriya INEC sa ido kan taron da ake sa ran za a zabi sabbin shugabanni na kasa.

Mai shari’a Peter Lifu ne ya bayar da wannan sabon umarni a ranar Talata, bayan sauraron karar tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, wanda ya koka cewa an hana shi damar siyan fom din neman shugabancin jam’iyyar.

Alkalin ya ce PDP ta saba doka da sharuddan da ake bukata wajen shirya irin wannan taro, inda ya kara da cewa rashin bibiya da bin tsarin doka na iya zama barazana ga dimokuradiyya a kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata