Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai‘Yan bindiga sun hallaka mai juna biyu a kauyen Alkalije da ke...

‘Yan bindiga sun hallaka mai juna biyu a kauyen Alkalije da ke Sokoto

Wasu ‘yan bindiga sun kai hari garin Alkalije da ke karamar hukumar Yabo a jihar Sakkwato, inda suka hallaka mutane biyar ciki har da mace mai juna biyu da safiyar Litinin.

Majiyoyi sun ce maharan sun afka garin ne da sassafe suna harbe-harbe, inda wasu mazauna kauyen biyu suka samu raunuka kuma aka garzaya da su asibiti.

Garin Alkalije na karkashin masarautar Kilgori kuma yana iyaka da karamar hukumar Silame da wasu yankuna na jihar Kebbi, inda ake zargin ta nan maharan ke shigowa.

Wani dattijo a yankin ya ce ‘yan bindigar sun saba kai farmaki daga Kebbi da Silame, suna hallaka mutane da sace wasu, har ma suna kakaba haraji kan al’umma, inda ya roki gwamnati ta kafa sansanin tsaro a yankin domin dakile hare-haren.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata