Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiMuna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko...

Muna biyan ‘yan bindiga Naira miliyan 7 don zama a gidajenmu ko noma gonakinmu

Wasu al’ummomi a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja sun bayyana cewa suna biyan haraji ga ‘yan bindiga domin su samu damar zama a garuruwansu ko kuma ci gaba da noma gonakinsu.

A cewar shugaban al’ummar, Alhaji Yahaya, wanda ya bayyana haka yayin wata hira da shi a shirin Tsalle Daya na tashar Prestige FM Minna, ya ce al’ummarsu ta na biyan ‘yan ta’adda Naira miliyan bakwai a matsayin kudi domin barinsu su zauna a mahalllansu.

Ya ce garuruwan da ke karkashin ikon ‘yan bindigar sun haɗa da Makera, Galapai, Chukuba, Ushaka, Manini, Kawuri, Bakarie I, Utako da Magana, inda kowane mutum mai aure ke ba da gudunmawa wajen tara kudin.

Ya ƙara da cewa ‘yan bindigar kan shigo cikin gari da bindigu har sai an ba su kuɗi, yayin da jami’an tsaro kuma suka daina yin sintiri a yankin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata