Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar da ta sake yin nasara.
Wannan mataki ya biyo bayan zarge-zargen magudi da gallazawa daga gwamnati da ‘yan adawa suka yi, lamarin da ya haddasa zanga-zanga mai muni tare da rasa rayukan daruruwan mutane.
Kungiyoyin kare hakkin dan adam da ‘yan adawa sun ce an halaka mutanen ne a lokacin da aka katse intanet baki ɗaya a kasar.
A jawabinta na farko a gaban majalisar bayan sake zabenta, Shugaba Samia ta umarci ‘yan sandan kasar da jami’an tsaro su sassauta wa matasa masu zanga-zanga.
