Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiGwamnonin PDP hudu sun isa Ibadan don gudanar da babban taron jam'iyyar

Gwamnonin PDP hudu sun isa Ibadan don gudanar da babban taron jam’iyyar

Gwamnonin PDP huɗu sun isa birnin Ibadan domin halartar babban taron kasa da jam’iyyar ta shirya, duk da hukuncin kotun tarayya da ta bayar na dakatar da taron.

Jaridar Punch, ta tabbatar da zuwan gwamnonin Bauchi, Bala Mohammed, Zamfara, Dauda Lawal, Adamawa, Ahmadu Fintiri, da na Oyo, Seyi Makinde, domin shirye-shiryen taron da ake son gudanarwa ranar Asabar 15 da Lahadi, 16 ga Nuwamba.

Jam’iyyar PDP na cikin rikici tsakanin bangaren Nyesom Wike da na shugaban riko Umar Damagum, yayin da kotuna daban-daban ke bayar da umarni mabambanta game da halaccin gudanar da taron.

A babbar kotun Abuja, mai shari’a Peter Lifu ya dakatar da taron bayan tsohon Gwamnan jigawa Sule Lamido, ya kai ƙara cewa an hana shi damar sayen fom ɗin takarar shugabancin jam’iyyar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata