Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya ce ya kai kara kotu ne domin kare haƙƙinsa a jam’iyyar PDP, tare da jaddada cewa ba zai halarci taron babbar jam’iyyar da za a gudanar a karshen mako ba.
Lamido ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels inda ya yi bayani kan dalilan daukar matakin.
Ya kara da cewa matakin kotu da ya dauka ba ya da wata alaka da rikicin jam’iyyar, illa kawai neman adalci da gyaran kuskuren da aka yi masa ne.
