Wednesday, April 8, 2026
HomeSiyasaJam'iyyar PDP ta kori su Wike daga cikinta

Jam’iyyar PDP ta kori su Wike daga cikinta

Jam’iyyar PDP mai hamayya a Nijeriya ta bayyana korar ministan birnin Abuja Nyesom Wike da wasu ‘ya’yanta daga cikinta.

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar na yankin kudancin Nijeriya Cif Olabode George ne ya gabatar da kudurin korar yayin babban taron jam’iyyar da ke gudana a birnin Ibadan na jihar Oyo.

Baya ga ministan Abuja Nyesom Wike, jam’iyyar ta kori tsohon sakatarenta Samuel Anyawu da tsohon gwamnan Ekiti Ayodele Fayose kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata