’Yan bindiga sun tare wata motar haya suka tafi da fasinjoji shida sannan suka kashe direba a hanyar Ogobia–Adoka da ke ƙaramar hukumar Otukpo a Jihar Benue, kamar yadda mazauna yankin suka bayyana.
Lamarin ya faru a ƙarshen mako, in ji shugaban ƙaramar hukumar Otukpo, Alfred Omakwu, wanda ya tabbatar da faruwar abin ta wayar tarho, yana mai cewa har yanzu ba a san matsayin fasinjojin ba sai dai jita-jitar cewa an fara tattaunawa da iyalansu.
Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun tilasta motar ta tsaya, abin da ya jawo ta shiga cikin daji kafin a tafi da fasinjojin zuwa wuri da ba a sani ba.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Benue, DSP Udeme Edet, ta ce za ta fitar da karin bayani daga baya, amma har zuwa lokacin wannan rahoto ba ta dawo da martani ba kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
