Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaJam'iyyar ADC ta sake bukatar rajistar su Atiku a hukumance

Jam’iyyar ADC ta sake bukatar rajistar su Atiku a hukumance

Jam’iyyar ADC reshen jihar Adamawa ta bukaci tsohon mataimakin shugaban Nijeriya Atiku Abubakar, da tsohon sakataren gwamnatin tarayya Babachir Lawal su yi rajistar zama mambobinta a hukumance.

Jaridar Punch ta ruwaito shugaban ADC na Adamawa Shehu Yohanna na yin wannan kira, yana mai cewa cikin makon nan Atiku Abubakar zai je jiharsa ta Adamawa don gabatar da bikin ranar haihuwa da kuma wasu al’amura.

[contact-form][contact-field label=”Name” type=”name” required=”true” /][contact-field label=”Email” type=”email” required=”true” /][contact-field label=”Website” type=”url” /][contact-field label=”Message” type=”textarea” /][/contact-form]

A cewar sa, yana sa ran Atiku Abubakar zai yi amfani da wannan dama don yankar tikitin zama cikakken dan jam’iyya.

Kafin wannan lokaci dai jam’iyyar ta ADC reshen Adamawa, ta sha bai wa su Atiku wa’adin yankar katin zama cikakkun mambobi, sai dai har zuwa wannan lokaci babu wani yunkuri daga manyan ‘yan siyasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata