DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sandan Abuja sun yi ajalin ‘yan ta’adda lokacin da suka dakile wani hari

-

Rundunar ‘yan sandan Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya ta dakile wani yunƙurin garkuwa da mutane da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne su kimanin 30 suka yi a kauyen Guto da ke karamar hukumar Bwari.

A cewar sanarwar da SP Josephine Adeh, kakakin rundunar ‘yan sandan ta aike wa DCL Hausa, ta ce ‘yan sandan sun yi ajalin biyu daga cikin maharan yayin da sauran suka tsere cikin daji.

Google search engine

Sai dai a yayin musayar wuta, wani ɗan sanda ya samu mummunar rauni, inda daga bisani likita ya tabbatar da rasuwarsa a asibitin Bwari.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Amnesty International ta koka kan halin da jihar Katsina ke ciki kan batun tsaro

Kungiyar kare hakin bil’adama ta Amnesty International ta gargadi cewa hare-haren ’yan bindiga da ƙungiyoyin ta’addanci suna tura Jihar Katsina zuwa ga mummunan bala’in jin-kai,...

Gwamnatin Sokoto ta kammala aikin samar da lantarki na kashin kanta na N7bn

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kammala aikin gina tashar samar da wutar lantarki ta mai zaman kanta, kamar yadda Kwamishinan Makamashi, Alhaji Sanusi Danfulani, ya bayyana...

Mafi Shahara