Sunday, April 5, 2026
HomeLabarai'Yan sandan Abuja sun yi ajalin 'yan ta'adda lokacin da suka dakile...

‘Yan sandan Abuja sun yi ajalin ‘yan ta’adda lokacin da suka dakile wani hari

Rundunar ‘yan sandan Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya ta dakile wani yunƙurin garkuwa da mutane da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne su kimanin 30 suka yi a kauyen Guto da ke karamar hukumar Bwari.

A cewar sanarwar da SP Josephine Adeh, kakakin rundunar ‘yan sandan ta aike wa DCL Hausa, ta ce ‘yan sandan sun yi ajalin biyu daga cikin maharan yayin da sauran suka tsere cikin daji.

Sai dai a yayin musayar wuta, wani ɗan sanda ya samu mummunar rauni, inda daga bisani likita ya tabbatar da rasuwarsa a asibitin Bwari.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata