Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiPantami ya ba gwamnatin Nijeriya shawarar yin amfani da fasahar zamani don...

Pantami ya ba gwamnatin Nijeriya shawarar yin amfani da fasahar zamani don yakar ayyukan ta’addanci

Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Dijital, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya bayyana damuwarsa bisa yawaitar hare-hare, kisa da kuma garkuwa da mutane da ake fuskanta a jihohin ƙasar nan, musamman Kebbi da Zamfara.

Tsohon Ministan sadarwa, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, ya yi tir da yawaitar tashe-tashen hankula a fadin Nijeriya, musamman hare-haren da ake yi da kuma garkuwa da mutane da dama a jihohin Kebbi da Zamfara.

A cikin wata sanarwa da ya fitar yana Allah wadai da abin bakin cikin, Pantami ya yi kira ga hukumomin gwamnati da su gaggauta rungumar sabbin dabaru na zamani da suka dogara ga fasaha domin yakar ta’addanci da kuma kare rayukan ‘yan kasa.

Pantami ya ce amfani da fasahohi na zamani zai taimaka wajen cafke masu aikata laifin, hana sake faruwar irin wadannan hare-hare, da kuma dawo da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci ’yan kasa su rika bada bayanan sirri da zai taimaka wa hukumomin tsaro wajen tunkarar miyagun laifuka.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata