Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiMatsayin da nake da shi a kungiyar dattawan Yammacin Afrika ya sa...

Matsayin da nake da shi a kungiyar dattawan Yammacin Afrika ya sa na janye daga harkokin siyasa – Jonathan

Tsohon Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, ya bayyana cewa zama memba a Dandalin Dattawan Afrika ta Yamma (WAEF) shi ne babban dalilin da ya hana shi komawa siyasa kai tsaye ko mara baya ga kowace jam’iyya.

A cewar Jonathan, yayin taron cika shekaru 10 da kafa Goodluck Jonathan Foundation (GJF) da aka gudanar a Abuja, kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito, dokokin dandalin na WAEF sun wajabta wa membobinsu su kasance masu ajiye ra’ayin siyasa ko bangaranci a gefe.

Jonathan ya bayyana WAEF a matsayin mai tsarin da ke kai ziyara ƙasashe a lokacin zaɓe domin shawo kan duk wani alamar tashin hankali tun kafin ya rikide ya zama rikici baki ɗaya.

Ya kuma yi tir da abin da ya kira “tashanci a siyasar Nijeriya”, yana kira ga ’yan siyasa su gudanar da harkokinsu cikin ladabi, hikima da ɗa’a domin kare mutuncin ƙasa da dimokuraɗiyya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata