Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiPDP tsagin Wike suna neman a soke taron da PDP tayi a...

PDP tsagin Wike suna neman a soke taron da PDP tayi a Ibadan

Jam’iyyar PDP tsagin Ministan Abuja Nyesom Wike, ta shigar da kara a gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, tana neman a soke taron jam’iyyar da aka gudanar a Ibadan ranar 15 da 16 ga Nuwamba, karkashin jagorancin Gwamna Seyi Makinde.

Mukaddashin shugaban jam’iyyar na tsagin, Mohammed Abdulrahman, da sakataren jam’iyyar Samuel Anyanwu, su ne masu shigar da karar, inda suke rokon kotu ta ayyana taron na Ibadan a matsayin harantacce tare da hana INEC amincewa da duk wani hukunci da aka yanke a taron.

Karar ta zo ne bayan wasu koke da tsoffin shugabannin jam’iyyar daga jihohi suka shigar, suna zargin cewa gudanar da taron ya saba wa dokokin PDP.

Cikin wadanda suka gabatar da koken akwai Shugaban PDP na Imo, Austin Nwachukwu, na Abia, Amah Abraham Nnanna, da Sakataren PDP na Kudu maso Kudu, Turnah Alabh George.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata