An kulle fadar White House, ta Amurka, tare da wasu muhimman gine-ginen gwamnati sakamakon harbin da aka yi kusa da fadar shugaban ƙasar.
An harbi sojoji biyu na National Guard a inda lamarin ya faru kamar yadda jaridar Daily Trust ta wallafa.
Gwamna Patrick Morrisey ya fara bayyana cewa an kashe dakarun, amma daga baya ya ce rahotannin da yake samu sun yi karo da juna game da halin da sojojin suke ciki, inda ya ƙara da cewa za a fitar da cikakken bayani idan an tabbatar.
