Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiJanye 'yansanda daga tsaron manyan mutane zai jefa mu cikin haɗari -...

Janye ‘yansanda daga tsaron manyan mutane zai jefa mu cikin haɗari – Sanatoci

Sanatoci da dama sun nuna damuwa kan umarnin Shugaba Tinubu na janye jami’an ’yan sanda daga tsaron manyan mutane, suna cewa matakin na iya barin su cikin barazanar tsaro.

Sanatocin sun bayyana wannan damuwar ne a zaman majalisar ranar Laraba yayin tattaunawa kan tabarbarewar tsaro, bayan gabatar da kudiri daga Sanata Oyelola Yisa Ashiru kan bukatar gaggawar duba lamarin daga gwamnatin tarayya.

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin a janye jami’an daga tsaron manyan mutane domin mayar da su kan ayyukan su na asali, lamarin da ya janyo cece-kuce a majalisar dattawa da ta wakilai.

A lokacin muhawarar, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko ya ce wannan mataki bai dace ba a lokacin da hare-haren ’yan bindiga ke karuwa, yana mai cewa jami’an gwamnati na daga cikin manyan da ke bukatar tsaro.

Shi ma Sanata Tahir Monguno daga Borno ya ce janye ‘yansandan daga jami’an gwamnati zai kara mayar da su abin hari, ganin yadda yanayin tsaro ke tabarbarewa a sassan kasar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata