Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAl’amura sun fara komawa daidai a Guinea Bissau

Al’amura sun fara komawa daidai a Guinea Bissau

Al’amura sun fara komawa daidai a Guinea Bissau bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa sojoji sun nada Janar Horta N’Tam, a matsayin shugaban na rikon kwarya na tsawon shekara guda bayan kifar da gwamnati a ranar Laraba.

Rahoton ya ce juyin mulkin ya faru ne kwana guda kafin a bayyana sakamakon zaben 23 ga Nuwamba.

A safiyar Juma’a, motocin haya a manyan tituna sun dawo zirga-zirga, shaguna da kasuwanni sun fara budewa, duk da cewa har yanzu an tsaurara tsaro a wasu muhimman wurare.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata