Tsohon Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan, ya ce abin da ya faru a Guinea-Bissau ba juyin mulki na gaske ba ne, illa dabara da Shugaba Umaro Embaló ya kitsa don kauce wa fitar da sakamakon zabe.
Jonathan, wanda ya je kasar a matsayin mai sa ido kan zabe, ya dawo bayan rikicin ya barke ya ce abin mamaki ne ganin Embaló shi ne ya fara sanar da cewa an yi juyin mulki, sannan yana magana da kafafen yada labarai cikin ‘yanci, alamar cewa lamarin ba gaskiya ba ne. Ya ce hakan ya fi masa ciwo fiye da lokacin da ya fadi zaben 2015.
Juyin mulkin ya faru ne kwana guda kafin a bayyana wanda ya lashe zaben da Embaló da Fernando Dias suka kara. Daga baya, Kwamandan sojojin kasa, Horta Inta-A wanda ake alakanta shi da Embaló ya kama mulki, yayin da Embaló ya gudu zuwa Senegal.
