Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiGwamnan jihar Kebbi ya gana da shugaba Tinubu bayan ceto daliban da...

Gwamnan jihar Kebbi ya gana da shugaba Tinubu bayan ceto daliban da aka sace a jihar Kebbi

Shugaba Bola Tinubu ya karɓi Gwamnan Kebbi, Nasir Idris, a fadar shugaban Nijeriya Abuja, inda suka tattauna kan ayyukan tsaro a Arewa maso Yamma da ceto ɗalibai ’yan makarantar GGCSS Maga da aka sace a ranar 17 ga watan Nuwamba.

Gwamnan ya gode wa Shugaba Tinubu bisa umarnin gaggawa da kuma yadda hukumomin tsaro da leƙen asiri na tarayya suka samu nasarar ceto ɗaliban a ranar 26 ga watan Nuwamba, kafin a miƙa su ga iyayensu a Birnin Kebbi. Ya kuma yaba wa ministan tsaro, Bello Matawalle, bisa jagorantar aikin ceton.

Taron ya zo ne a lokacin da ake fama da sake ƙaruwa da garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, musamman hare-haren da ke nufi a makarantu kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata