Sunday, April 5, 2026
HomeSiyasaA binciki musabbabin ibtila'in da ya afku a kasuwar Singa jihar Kano...

A binciki musabbabin ibtila’in da ya afku a kasuwar Singa jihar Kano – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya jajanta wa ‘yan kasuwa da al’ummar jihar Kano kan mummunar asarar ‘yan kasuwa suka yi a kasuwar Singer a karshen mako.

A yammacin ranar Asabar ne, wuta ta tashi a kasuwar har zuwa safiyar Lahadi, inda ta yi barna mai yawa a sashen kasuwar kayan abinci.

Shugaban kasar, wanda tun da fari ya tuntubi Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, domin samun rahoton halin da ake ciki, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

Shugaba Tinubu ya ba da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan musabbabin tashinta, wanda ke yawan jefa ‘yan kasuwa cikin halin kunci kamar yadda Bayo Onanuga mai magana da yawunsa ya sanar.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata