Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAbin kunya ne rufe makarantu a Arewa saboda matsalar tsaro - Buba...

Abin kunya ne rufe makarantu a Arewa saboda matsalar tsaro – Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar NNPP Buba Galadima, ya soki matakin wasu gwamnatocin Arewa na rufe makarantu saboda karuwar sace-sacen dalibai, yana bayyana matakin a matsayin abin kunya da rashin hangen nesa.

Buba Galadima ya furta haka ne a lokacin da yake hira a gidan talabijin na Arise a inda ya ce matsalar tsaro da ta kunno kai musamman a jihar Neja da sauran jihohi ba dalili ba ne da zai sa a tsaida karatu.

Ya jaddada cewa abin da ya kamata shi ne ƙarfafa tsaro a makarantun da ke fadin Arewa, tare da yin amfani da fasahohin zamani wajen gano barazana tun kafin ta faru.

A cewarsa yawancin hare-haren na faruwa ne saboda rashin amfani da bayanan sirri da ake samu da wuri.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata