Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAbinda na gaya wa Shugaba Tinubu kan ziyarata a Nijar - Abdulsalami...

Abinda na gaya wa Shugaba Tinubu kan ziyarata a Nijar – Abdulsalami Abubakar

Tsohon shugaban
Najeriya Abdulsalam Abubakar ya sanar da mikawa shugaban kasar Bola Ahmad
Tinubu rahoto kan batutuwan da suka tattauna yayin ziyarar tawagar da ya
jagoranta zuwa jamhuriyar Nijar.

Da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan
kammala ganawar sa da shugaban kasa, Abdulsalam Abubakar ya ce dukkanin alamu
sun nuna cewa yaki ba zai shawo kan al’amarin ba, a maimakon haka kamata ya yi
a rungumi tattaunawar diplomasiyya.

Ganawar ta su ta sami halarcin shugaban majalisar
zartaswar kungiyar ECOWAS Dr Omar Touray da kuma babban mai baiwa shugaban
Najeriya shawara kan harkokin yada labarai Malam Nuhu Ribadu.

Bayan kammala ganawar ta su, shugaban Najeriya Tinubu
wanda kuma shine shugaban ECOWAS ya sha alwashin yiwa rahoton Nazari na tsanaki,
kafin daga bisani kuma a san matakin da za’a dauka.

Wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ECOWAS ta
sanar da cewa ta gama duk wani shiri na fadawa Nijar da yaki.

 

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata