Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAdadin mutanen da suka rasa rayukansu a hatsarin Kwale - kwale a...

Adadin mutanen da suka rasa rayukansu a hatsarin Kwale – kwale a Yobe ya karu zuwa 29

Adadin mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon hatsarin kwale-kwale da ya faru a karamar hukumar Nguru ta jihar Yobe ya ƙaru daga 25 zuwa 29, kamar yadda hukumomin jihar suka sanar.

Sakatare a hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Yobe (YOSEMA), Dakta Mohammad Goje, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Damaturu a ranar Litinin.

Ya ce an ƙara gano gawawwaki huɗu daga cikin kogin, yayin da mutane tsakanin 8 zuwa 10 har yanzu ake neman su, ya ƙara da cewa fasinjoji 13 da suka jikkata a hatsarin an ba su magani kuma an sallame su daga asibiti.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata