Jam’iyyar adawa ta ADC ta bukaci Farfesa Joash Amupitan ya sauka daga shugabancin INEC, tare da yin barazanar sake shiga zanga-zanga idan hakan bai faru ba.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito jam’iyyar ta bayyana haka ne yayin da take martani kan sabbin zarge-zarge da ake yi masa.
ADC ta zargi Amupitan da nuna bangaranci ga jam’iyyar APC, bisa wasu tsofaffin sakonnin da ake zargin ya wallafa a shafin sada zumunta.
Kodayake mai magana da yawun shugaban INEC, Adedayo Oketola, ya gargadi jama’a kan masu kirkirar asusu na bogi da ke yada bayanan karya domin bata sunan maigidansa.
