Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAkpabio ya ba mata kyautar kwale-kwalen kamun kifi a matsayin barka da...

Akpabio ya ba mata kyautar kwale-kwalen kamun kifi a matsayin barka da Kirsimeti

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya Sanata Godswill Akpabio ya bayar da kyautar kwale-kwalen kamun kifi masu amfani da inji guda 10 ga mata a mazabarsa ta Akwa Ibom ta Kudu.

 

Cikin wata sanarwa da ofishin yada labarai na Sanatan ya fitar, Akpabio ya bayar da kyautar ne a garinsa na Ukana, karamar hukumar Essien Udim da ke jihar, a matsayin kyautar barka da ranar Kirsimeti.

 

Sanarwar ta ce an zabo wadanda aka bai wa kyautar ne daga yankunan da suke da koguna, inda ake yawan gudanar da sana’ar kamun kifi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata