Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya daukaka kara a Kotun Daukaka Kara da ke Abuja domin kalubalantar hukuncin da wata babbar kotu ta tarayya ta yanke na maido da Senata Natasha Akpoti-Uduaghan.
Rahoton jaridar Daily Trust ya ruwaito yadda kotun ta yanke hukunci a ranar 4 ga Yuli cewa dakatarwar wata shida da aka yi wa Natasha ta yi yawa, tare da tilasta biyan ta Naira miliyan biyar saboda wani rubutu da ta wallafa a shafin sada zumunta yayin da karar ke gudana.
A cikin korafinsa na hujjoji 11, Akpabio ya bukaci kotun daukaka karar ta soke hukuncin, yana mai cewa kotun farko ta sauka a layi, inda ta shiga hurumin shari’a kan harkokin cikin gida na Majalisar Dokoki kamar yadda kundin tsarin mulki na kasa (Sashe na 251) ya tanada.
