Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAkwai bukatar sake duba yarjejeniyar bashin da NNPCL ya ciyo wa Nijeriya...

Akwai bukatar sake duba yarjejeniyar bashin da NNPCL ya ciyo wa Nijeriya – Gwamnatocin jihohi

Gwamnatocin jihohin Nijeriya sun bukaci a sake duba tsarin bashin da kasar ke biya da danyen mai na Dala Biliyan 8

Rahotanni sun nuna cewa kamfanin NNPCL ya jinginar da ganga dubu 272,500 na danyen mai a rana domin karbar bashin da ya kai dala biliyan 8.86. wanda daga ciki aka biya kusan dala biliyan 2.61, yayin da ake bin Nijeriya sama da dala biliyan 6.

Bukatar binciken ta fito ne daga taron kwamitin rarraba asusun tarayya da aka gudanar a Enugu, inda jami’an gwamnati da kwararru suka tattauna hanyoyin dakile asarar kudaden shiga da ke shafar raba kudaden tsakanin matakan gwamnati uku.

Mahalarta taron sun bukaci duk wata yarjejeniya ta bashin danyen mai ta samu amincewar majalisa, a bayyana cikakkun bayanai game da ita, sannan a gudanar da bincike mai zaman kansa domin kare kudaden Asusun Tarayya.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata