Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAkwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye -...

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma wasu majiyoyi sun ce ya koma Abuja a ruwaitowar jaridar Daily Trust.

Rahoton ya ce an fitar da shi daga gidansa da ke Marouaré a Garoua tsakanin 28 da 29 ga watan Oktoba inda a sakonsa na Facebook, ya gode wa sojojin da suka raka shi zuwa wuri mai aminci.

A cewar rahoton, an tsallaka da shi zuwa Nijeriya bayan fargabar kai masa hari daga jami’an tsaro yayin da a safiyar 29 ga watan Oktoba, aka ji harbe-harbe a unguwarsa.

Ministan harkokin cikin gida, Paul Atanga Nji, ya gargade shi kan tada rikicin bayan zabe, yana mai cewa ya karya doka da ya ayyana kansa a matsayin wanda ya lashe zabe kafin sakamakon hukuma ya fita.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata