Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiAlƙali ya yi barazanar soke belin Abdulrasheed Maina da ake zargin kan...

Alƙali ya yi barazanar soke belin Abdulrasheed Maina da ake zargin kan zambar N738.6m

Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke Abuja, ta yi barazanar soke belin tsohon shugaban kwamitin garambawul a harkar fansho na ƙasa, Abdulrasheed Maina, bisa zargin yin dabaru daban-daban domin jinkirta shari’arsa.

Alƙali Abubakar Kutigi ya nuna ɓacin rai ne yayin zaman kotu da aka gudanar Alhamis, 5 ga Fabrairu, 2026, bayan lauyan Maina ya gabatar da takardar tura shi asibiti tare da neman dage shari’a, duk da cewa takardar ba ta nuna wata babbar rashin lafiya ba, kamar yadda shafin hukumar EFCC ya ruwaito.

Alƙalin ya ce shari’ar ta yi shekaru huɗu ana jan ƙafa, sakamakon abin da ya kira dabarun Maina na jinkirta shari’a, inda ya bayyana cewa Maina bai halarci kotu ba tun shekaru huɗu da suka gabata.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata