Hukumar kwallon kafa ta kasar Aljeriya FAF, ta tabbatar da cewa ta miƙa ƙorafi ga hukumar kwallon kafa ta Afirka (CAF) da kuma hukumar kwallon kafa ta duniya (FIFA) dangane da hukuncin alkalan wasa a wasan da ta buga da Nijeriya.
A wata sanarwa da suka wallafa shafin X na tawagar ƙwallon ƙafar Aljeriya, FAF ta ce ta nemi a fara bincike na musamman domin a fayyace hukuncin da aka ce sun tayar da rigima, tare da ɗaukar matakin da ya dace bisa ƙa’ida.
A cewar FAF, ba ta gamsu da wasu hukunce-hukuncen alkalai a wasan ba, sabkda shakku da rashin gamsuwa da hakan ke haifarwa ga alkalancin wasanni a Afirka.
