Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAmnesty International ta soki yadda Hukumar DSS ke kama mutane saboda fadin...

Amnesty International ta soki yadda Hukumar DSS ke kama mutane saboda fadin ra’ayinsu kan rikicin Iran, Amurka da Isra’ila

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta nuna damuwa kan abin da ta kira kara tsaurara mataki da Hukumar farin kaya ta DSS ke yi kan masu yin sharhi a kafofin sada zumunta game da yakin Gabas ta Tsakiya.

Kungiyar ta ce akalla mutane biyu mazauna Kaduna an tsare su, kuma ana shirin gurfanar da daya daga cikinsu a kotu bisa tuhume-tuhumen da ta kira marasa tushe.

A cewar kungiyar, sukar manufofin gwamnatocin Amurka ko Isra’ila hakki ne na ‘yancin fadin albarkacin baki da kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada, don haka ta bukaci hukumomin kasar su mutunta wannan hakki ba tare da tsoratar da masu ra’ayi ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata