Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAmurka ta ba da tallafin Dala miliyan 5 domin ceto yara masu...

Amurka ta ba da tallafin Dala miliyan 5 domin ceto yara masu fama da tamowa a Nijeriya

Kasar Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 5 ga asusun kula da yara na majalisar dinkin duniya (UNICEF) domin kai agajin gaggawa ga yara masu fama da rashin abinci mai gina jiki a Arewa maso Yammacin kasar.

Sanarwar da ofishin jakadancin Amurka ya fitar ranar Alhamis ta ce kudin za su taimaka wajen kai tallafi ga akalla yara 70,000.

UNICEF za ta yi amfani da kuɗin wajen samar da abinci mai inganci kai tsaye, magunguna da sauran muhimman kayayyakin jin-kai.

Wannan taimako na daga cikin matakan Amurka na tallafa wa ƙoƙarin rage matsananciyar yunwa da inganta lafiyar yara a yankin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata