Monday, April 6, 2026
HomeKetareAmurka za ta kori ’yan Nijeriya 79 da suka aikata manyan laifuka

Amurka za ta kori ’yan Nijeriya 79 da suka aikata manyan laifuka

Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida ta Amurka ta bayyana cewa za ta kori ’yan Nijeriya ba ƙasa da 79 da aka yanke wa hukunci bisa aikata laifuka a ƙasar.

Binciken jaridar PUNCH a shafin yanar gizon DHS a ranar Litinin ya nuna cewa ’yan Nijeriyan 79 din sun samu hukunci ne kan laifuka da suka haɗa da zamba, fataucin miyagun ƙwayoyi, duka da raunatawa, kisan kai da fashi, da sauransu.

Wata sanarwa ta nuna cewa an kama mutanen ne a cikin yakin da Amurka ke yi na kama ’yan ƙasashen waje masu aikata laifuka, kafin a shirya korarsu daga ƙasar.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata