Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAmurka za ta koro karin 'yan Nijeriya 19 gida kan aikata munanan...

Amurka za ta koro karin ‘yan Nijeriya 19 gida kan aikata munanan laifuka

Gwamnatin Amurka ta kara sanya sunayen ‘yan Nijeriya 19 cikin kundin masu munanan laifuka, yayin da ta ke shirin kora su gida.

Wasu bayanai daga shafin yanar gizo na ma’aikatar tsaron cikin gidan Amurka sun nuna cewa mutanen da aka kara, sun sa adadin wadanda za a kora gida ya kai 113.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa laifukan da ‘yan Nijeriyar suka aikata sun hadar da safarar miyagun kwayoyi, cin zarafi, damfara da wasu miyagun laifuka.

Ma’aikatar tsaron ta bayyana cewa da zarar ta kammala bin matakan da suka dace, za ta kora mutanen gida.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata