Tuesday, April 7, 2026
HomeLabaraiAn damfari wata mata kudi N603m don a bata aiki a kamfanin...

An damfari wata mata kudi N603m don a bata aiki a kamfanin NNPCL

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Nijeriya, EFCC ta gurfanar da Gidado Ibrahim a gaban Kotun Babban Birnin Tarayya Abuja, bisa zargin damfarar kudade har N603.4m, inda ake zargin ya karbi kudin ne da sunan shirya wa wata mace mukamin Shugabar Kamfanin Man Fetur na Nijeriya NNPC.

A zaman kotun na ranar Litinin, alkalin kotun Mai shari’a H. Muazu ya karanto tuhuma guda shida da suka shafi damfara da amfani da takardun bogi, ciki har da amfani da wata takarda mai taken “ofishin mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro” da ake zargin ta bogi ce.

Gidado Ibrahim ya musanta dukkan tuhume-tuhumen, lamarin da ya sa kotu ta dage shari’ar zuwa 17 ga Fabrairu, 2026, tare da umarnin a tsare shi a gidan yarin Kuje, yayin da ake jiran sauraron bukatar belinsa.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata