Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAn kama mabarata 210 a titunan Abuja - Hukumar FCTA

An kama mabarata 210 a titunan Abuja – Hukumar FCTA

Hukumar raya babban birnin tarayya Abuja (FCTA) ta ce an kama mutane 210 da ake zargi da barace-barace da wasu laifuka daban-daban, a wani sabon yunkuri da take kawar da barace-barace daga titunan Abuja.

Daraktar rikon kwarya ta sashen jin ƙai da kula da walwalar jama’a, Gloria Onwuka, ce ta bayyana hakan yayin miƙa waɗanda aka kama zuwa cibiyar gyaran halaye da ke Bwari, a cewar gidan talabijin na NTA.

Gloria ta ce waɗanda aka kama sun haɗa da mata, maza da yara waɗanda ke barace-barace a manyan tituna, da kuma wasu da ake zargi da aikata laifuka daban-daban.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata