Monday, April 6, 2026
HomeLabaraiAn kama wasu ƴan Nijeriya 3 kan zargin aikata damfara ta yanar...

An kama wasu ƴan Nijeriya 3 kan zargin aikata damfara ta yanar gizo a Kenya

Rundunar da ke gudanar da binciken manyan laifuka a ƙasar Kenya (DCI) ta tabbatar da kama wasu ’yan Nijeriya uku bisa zargin aikata damfara ta yanar gizo.

Jaridar Punch ta rawaito cewa, jami’an DCI sun kama mutanen ranar Laraba, bayan al’ummar yankin sun shigar da korafi kan motsin mutanen da suke gani a daren cikin wani gida da basu amince da shi ba.

DCI ta bayyana cewa mutanen uku sun ce suna gudanar da kasuwanci na intanet, sai dai an gano cewa suna zaune ne a kasar ba bisa ka’ida ba, kuma ba tare da samun lasisin aiki a kasar ba.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata