Monday, April 6, 2026
HomeKetareAn naɗa mace ta farko a matsayin Firaministan Nepal bayan kwanaki ana...

An naɗa mace ta farko a matsayin Firaministan Nepal bayan kwanaki ana zanga-zanga

An fara samun kwanciyar hankali a kasar Nepal bayan da aka nada mace ta farko a matsayin Firaminista na wucin gadi, jim kadan bayan tarzomar zanga-zangar cin hanci da rashawa da ta girgiza kasar.

A ranar Asabar ne babban birnin kasar ya fara komawa daidai, inda aka sassauta dokar hana fita bayan kwanaki da dakarun soja suka mamaye tituna tun ranar Laraba, lokacin da zanga-zangar ta yi sanadin kifar da gwamnati tare da kona majalisar dokokin kasar.

Akalla mutane 51 ne suka rasa rayukansu a wannan tarzoma, mafi muni tun bayan yakin basasa na tsawon shekaru goma da kuma rushe tsarin sarauta a shekarar 2008.

A daren Juma’a, an rantsar da tsohuwar alkalin kotun koli mai shekaru 73, Sushila Karki, a matsayin Firaminista na wucin gadi, domin aikin dawo da doka da oda da kuma sauraron bukatun masu zanga-zangar da ke neman kawar da cin hanci da rashawa.

Bayan haka, an rusa majalisar dokoki, aka kuma ayyana ranar 5 ga Maris, 2026 a matsayin ranar zabe, tare da soma kokarin gina sabuwar gwamnati.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata