An fara samun kwanciyar hankali a kasar Nepal bayan da aka nada mace ta farko a matsayin Firaminista na wucin gadi, jim kadan bayan tarzomar zanga-zangar cin hanci da rashawa da ta girgiza kasar.
A ranar Asabar ne babban birnin kasar ya fara komawa daidai, inda aka sassauta dokar hana fita bayan kwanaki da dakarun soja suka mamaye tituna tun ranar Laraba, lokacin da zanga-zangar ta yi sanadin kifar da gwamnati tare da kona majalisar dokokin kasar.
Akalla mutane 51 ne suka rasa rayukansu a wannan tarzoma, mafi muni tun bayan yakin basasa na tsawon shekaru goma da kuma rushe tsarin sarauta a shekarar 2008.
A daren Juma’a, an rantsar da tsohuwar alkalin kotun koli mai shekaru 73, Sushila Karki, a matsayin Firaminista na wucin gadi, domin aikin dawo da doka da oda da kuma sauraron bukatun masu zanga-zangar da ke neman kawar da cin hanci da rashawa.
Bayan haka, an rusa majalisar dokoki, aka kuma ayyana ranar 5 ga Maris, 2026 a matsayin ranar zabe, tare da soma kokarin gina sabuwar gwamnati.
An naɗa mace ta farko a matsayin Firaministan Nepal bayan kwanaki ana zanga-zanga
Recent Comments
on Gwamnatin Tinubu za ta fara ba da rancen maras kuɗin ruwa ga manoma da masu ƙananan sana’o’i – GEEP
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030
on Jaridar Daily Trust ta gano dalilai uku da suka sa Ganduje ya ajiye mukamin shugabancin APC na kasa
on Peter Obi ya sake jaddada bukatar kafa tsarin wa’adin shekara 5 kacal ga shugaban ƙasa a Najeriya
on Cire tsoffin ‘yan sanda daga daga tsarin Contributory Pension Scheme ya fi karfina – IGP Egbetokun
on Gwamnatin Nijeriya ta ɗage buɗe shafin neman aiki na Immigration, Civil Defence da sauran hukumomi
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3
on APCn jihar Kebbi ta yafe wa hadimin gwamna da aka dakatar saboda ya zo da maciji a fadar gwamnati
on An karkatar da Naira Bilyan 71.2 daga cikin Bilyan 100 na bashin dalibai a Nijeriya – Hukumar ICPC
on Gwamna Abba Gida Gida ya zabi tsohon shugaban ma’aikatansa da wasu mutum 5 a matsayin kwamishinoni
on Nijeriya za ta zama jagorar kasuwar halal ta duniya mai jarin Dala bilyan Dubu 7 – Kashim Shettima
