Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAn sace mutane a karamar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi, kwanaki...

An sace mutane a karamar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi, kwanaki kadan bayan an ceto dalibai ‘yan mata na makarantar Maga

Kwana guda bayan ceto ɗalibai mata 24 daga hannun ’yan bindiga, an sake samun rahoton sace mutane da dama a ƙauyen Kurmaci da ke Ƙaramar Hukumar Danko-Wasagu a Jihar Kebbi.

’Yan bindigar, kimanin su fiye da 30, sun kai farmaki a daren Laraba lokacin da mazauna yankin ke barci.

A yayin harin, an sace mutanen da ba a tantance adadinsu ba, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Wani mazaunin yankin Aliyu Dangaladima ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa, wannan hari shi ne na uku da ƙauyen ya fuskanta cikin wata guda.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata