Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAn shiga ruɗani bayan fashewar wasu abubuwa a jihar Kwara

An shiga ruɗani bayan fashewar wasu abubuwa a jihar Kwara

Al’ummar yankin Offa a jihar Kwara sun shiga fargaba a daren Alhamis bayan jerin fashewar abubuwa masu ƙarfi da suka girgiza wasu sassan garin, lamarin da ya lalata gidaje da shaguna a yankunan Yidi da Adeleke.

 

Jaridar Daily Trust ta ambato shaidu sun ce fashewar ta faru ne da tsakar dare, inda ta bazu har zuwa al’ummomin da ke makwabtaka saidai ba a tabbatar da asarar rai ba zuwa lokacin hada wannan rahoto.

 

An gano wasu abubuwan fashewa da ba su tashi ba, abin da ya ƙara tayar da shakku kan yiwuwar alaƙa da hare-haren jiragen sama marasa matuƙa na Amurka.

 

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kwara ta ce ana ci gaba da bincike domin gano ainihin musabbabin lamarin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata