Monday, April 6, 2026
HomeSiyasaƳan adaidaita ne suka yi jigilar kayan zaben kananan hukumomin Abuja

Ƴan adaidaita ne suka yi jigilar kayan zaben kananan hukumomin Abuja

An tura babura masu kafa uku da aka fi sani da Keke NAPEP domin jigilar muhimman kayayyakin zabe na INEC zuwa rumfunan zabe a zaben kananan hukumomin Babban Birnin Tarayya (FCT).

An ga kekunan na tsaye a wasu cibiyoyin rarraba kaya, inda jami’an zabe ke tabbatar da an kulle akwatunan zabe da takardun sakamako yadda ya kamata kafin a tura su zuwa unguwanni daban-daban a fadin Abuja.

Jaridar The Nation ta ruwaito amfani da Keke NAPEP na zama hanya mai sauki kuma mai rahusa wajen kai kayan zabe zuwa matakin karshe, musamman a wuraren da manyan motoci ke fuskantar cunkoso ko matsalar shiga.

Ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu rahotannin koke-koke masu yawa dangane da rarraba kayan zaben a FCT, duk da cewa masu sa ido na ci gaba da bibiyar yadda ake gudanar da aikin domin kauce wa jinkiri ko wata tangarda.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata