Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet, ta yi hasashen cewa a wasu sassan kasar za a fuskanci yanayin hazo na kwanaki uku a fadin Nijeriya.
A cewar hukumar, ana sa ran hazo da kura mai zai mamaye yawancin yankin Arewa ta Tsakiya a cikin wannan lokaci.
NiMet ta kuma bayyana cewa a yankin kudancin kasar za a samu rana tare da gajimare kadan, amma akwai yiwuwar samun tsawa da ruwan sama mai da yamma ko dare a wasu jihohin.
