Sunday, April 5, 2026
HomeLabaraiAna ci gaba da neman wata dattijuwa bayan kifewar kwale-kwale dauke da...

Ana ci gaba da neman wata dattijuwa bayan kifewar kwale-kwale dauke da fasinja 11 a Sokoto

An gano gawar wani matashi mai shekara 29 da ya rasa ransa a wani hatsarin jirgin ruwa da ya afku a Jihar Sokoto.

Lamarin ya faru ne ranar Juma’a a karamar hukumar Shagari ta jihar, a jirgin da ya dauki mutum 11, inda tuni aka ceto mutum 9 yayin da ake neman wata dattijuwa.

Mai bai wa Gwamna Ahmed Aliyu shawara na musamman a hukumar SEMA ta jihar, Aminu Bodinga, ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai, inda ya ce hatsarin ya afku ne ranar Alhamis.

Ya kara da cewa jami’an SEMA sun isa wurin domin gudanar da aikin ceto da kuma binciken wadanda suka bata.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttps://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Manajan Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.
RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata